Help Munir Overcome Brain Tumor Portal Closure

unnamed (12)
Munir and his brother Mubarak took a selfie at Well Care, Kano.

From Suleiman Garba Sule (emlanis)
As we’re running out of time and the Help Munir Overcome Brain Tumor portal at donate-ng.com is stagnant, HausaTrends Team (Faisal Abdullahi, Suleiman Garba Sule) has requested to withdraw the donated funds in Balance Due and terminate the campaign on the donate-ng website as there’s still some days left for the campaign to finish.
The funds have been directly transferred to Mannir Babangida’s UBA Bank account number 2064514554.
Even though the Hausatrends Team does not meet its target (only about 4% of ₦5,000,000), we really appreciate the kind gesture by the 38 kind-hearted givers who donated the sum of ₦178,800. Surely, your positive influence will help the confident, zero-worried Munir beat the dangerous brain tumor.

Munir is heading to Cairo…
The good news is that Munir is always grateful to God. He’s in high spirit, vibrant with full of positive energy. He’s a brave lad,super confident in his future. His brain is 1000% sharper and stronger than mine. It’s amazing. Munir is an inspiration in this kind of cancer battle. He reminds me of brother Ali Banat (May his precious soul rest in peace).
The good news is always good. At first, we made an attempt to admit Munir to Apollo Hospital in New Delhi and they’ve charged us $28,000 first things first. That’s at least N10.2 million! It wasn’t actually easy for Munir’s family to raise this kind of money after spending more than N5 million at the National Hospital Abuja. But you know what? God always has different ways to help His servants in need. Yes, there’s a hospital in Cairo, Egypt, that will work on Munir’s metastatic brain tumor for around N3.5 million! This hospital gives more than 50% discount on their normal charges. This is a super donation.
Door to donate in order to help Munir beat this scary brain tumor is still open. His bank account detail is: Mannir Babangida UBA Bank 2064514554.
With love and compassion,
HausaTrends.

Image

Doing a Good Deed Like a Smile :)

In this worldly life, any human being has at least a very small chance of helping another human being. A person can help another in many ways. From the smallest to the biggest.
If you make a person smiles by smiling at them just for the happiness of being, you have no clue how much you help them conquer a positive energy in their life. Negative energy is very inhuman and bad we all should avoid getting attracted to it.
Prophet Muhammad (PBUH) teaches us to smile and exchange greetings by saying ‘Assalamu Alaikum’ ( peace be unto you) because these two things are magnificent in helping and uniting us in one way or another.
You walking on street and see something harmful, you stop, take that thing, and park it in a place where nobody can get harmed. Do you realize that you do not help only one person but the whole society in general? That is so positive. You prevent your society from getting negative energy. Your society will be quite positive and healthy. That is what prophet Muhammad (PBUH) teaches us.
You see, any person in this world can do good and any good act somebody does will definitely help in one way or another.
You have a little knowledge of something good and you spread it to other people, there is no need to highlight how you help them a lot because you know you do.
I discover that I can help my society with anything I have but there is a need for me to wake-up and stand strong in order to do that important thing. Yes, I need to have the courage to give-out something, no matter how small is it, to people.
There is NO need for me to be like Bill Gates or Aliko Dangote in order to be able to help people. I can satisfactorily help them with the little I have. I can help them in any way I can because I want to make them happy not sad, I want to help them smile not cry. Oh yes, I can help them just for the sake of Allah.

Ƙa’idojin Motsa Jiki

Ƙa’idojin Motsa Jiki

Mukan yawaita cewa motsa jiki yana daya daga cikin abubuwan da mutum zai rika yi domin ya samu cikakkiyar lafiya. Hasali ma mukan ce ban da cin abinci mai lafiya, motsa jiki shi ne na biyu a muhimmanci wajen kiyaye cututtuka. 
Don haka muke ba su fifiko. Mun riga mun ga amfanin motsa jiki a wannnan shafi. Da yawa akan aiko tambayoyi a kan hanyoyi da ire-iren motsa jikin da ya dace mutum ya yi. A yau zamu yi bayani a kan ka’idoji da hanyoyi da kuma ire-iren motsa jiki da ya dace da mu.
Hukumar Kiyaye Cututtuka ta Duniya wato CDC da ke kasar Amurka, ta yi makala a kan wannan batu kuma za mu mai da hankali ne a kan abubuwan da ta ce a cikin wannan bayani.
Da farko aka ce ana so kafin mutum ya ce zai fara aikin motsa jiki, ya tabbatar ba shi da wani ciwon zuciya ko na hawan jini ko na sanyin kashi ko na asma. Idan yana da daya daga cikin wadannan, sai likita ya ba shi izini, da kuma nau’in da ya dace da shi. 
Mazan da suka kai shekaru 45 ko matan da suka haura shekaru 55, masana suka ce sai dole likita ya duba lafiyarsu kafin su fara wani nau’i na motsa jiki. 
Dole kuma a kudure cewa fa za a fara ne ba tare da fashi ba, wato ba kiwa, domin idan aka fara aka daina cikin kankanin lokaci to an rasa fa’idar. Wannan kiwa ce takan sa mutane rajista da kulab na motsa jiki ko wata kungiya ta wasanni.
To na’ukan motsa jikin nawa ne? Masanan suka ce akwai nau’i uku: 
Akwai mai kara kwarin jiki wato tsoka da kasusuwa (aerobic) kamar daukar nauyi da ire-irensu, da mai kara lafiyar zuciya da huhu (cardio) kamar gudu ko tafiya mai sassarfa ko tukin keke da ire-irensu, da kuma mai gyara daidaito da yadda gabobi ke motsi kamar ibadar Sallah, da ta yoga da tai chi.
Suka kara da cewa shi nau’i mai wuya, wato irin na aikin daga nauyi, a kan so akalla a yi mintuna 10 a rana ana yi. 
Shi kuma nau’i na biyu mai kara kaifin aikin zuciya, sai an shafe akalla mintuna 15 a rana ana yi kafin a samu fa’idar abin. 
Amma an fi son yin duka biyun ma domin mutum ya samu duka fa’idojin da akan samu. Nau’i na uku kusan kowa yana yi yau da kullum.
A cikin rana guda kuma lokacin da mutum ya kamata ya motsa jiki, ya danganta da son rai.
 Wasu sun fi so su yi da safe, wasu sun fi so su yi da yamma, wasu ma sun fi so su yi da dare.
 Masana suka ce ba wani bambancin lokaci da zai shafi motsa jiki da zai kawo matsala, amma masu yi da sassafe sun fi samun barci mai dadi idan dare ya yi, kuma masu yi da yamma sun fi samun kuzari da karfin ci gaba da motsa jikin.
Ana so kuma kafin mutum ya fara motsa jiki mai karfi ya dan sanarwa jikinsa cewa za a fara aiki. Idan gudu zai yi ya fara da sassarfa, idan nauyi zai daga ya fara da naushin iska misali, kafin a tsunduma ciki sosai. 
Ana kuma so idan an zo karshe a dan sassauta karfin motsa jikin, a sanar da jiki cewa an kusa gamawa. 
Duk wannan yana da alfanu ga lafiyar zuciya da ta tsoka, tunda wasu da sun fara gudu farat daya, nan da nan tsokar cinya kan daure, a samu muscle pull mai ciwo.
Sai shan ruwa. Ana so mutum ya sha akalla lita guda ta ruwa kamar minituna 30 kafin motsa jiki mai karfi, idan lokacin zafi ne ma zai iya sha fiye da haka. 
Ba dai a so mutum ya zo motsa jiki a ji ruwa na gulub-gulub a cikinsa shi ya sa ake sha da wuri. Idan motsa jikin ya wuce minti 30 kamar na ’yan kwallo shi ma sai an kawo ruwa a tsakankani ko ma irin lemon nan mai kara kuzari, wanda masana suka ce yana da amfani idan mutum zai motsa jiki na fiye da awa guda a lokaci daya.
To ya mutum zai gane yana samun fa’idojin? A nau’i na farko mai dan wahalar, mai yi zai ji bugun zuciya ya karu ko ma ya nunka. 
Wato idan mutum zuciyarsa na bugawa sau 80 a minti guda za ta iya kaiwa 160 idan yana motsa jiki mai karfi, idan sau 70 take bugawa a cikin minti guda, za ta iya kaiwa 140 ko ma 150 idan yana motsa jikin. Idan yana so ya yi furuci kuma kalmomi biyu ko uku ne kawai ke iya fita daga bakinsa yayin motsa jiki. 
Da yawa kuma za su ji zufa na karyo musu.
Ke nan idan mutum na motsa jiki amma bugun zuciyarsa bai karu ba, ko numfashinsa bai karfi ba, ba ya samun alfanun da ya kamata. 
Namiji mai sana’ar tsaye, kamar aski ko gugar kaya ko mace mai tafiya a hankali za ta wata anguwa ko wadda ke tsaye a shagon sai da kayayyaki na tsawon lokaci duk ba motsa jiki suke ba a bayanin masanan. 
Sai mutum ya yi wani abu da ya daga bugun zuciya, ya kuma kara karfin numfashinsa na tsawon akalla mintuna goma ake cewa ya amfanu da motsa jiki.
Kada kuma mutum ya zabi motsa jiki wanda zai sa ya rage teba a wani bangare na jiki kamar a mara. Mutane da dama sukan ce su sun fi so kawai su rage teba a mara, abin da wasu ke cewa tumbi, amma ba sa so su rage kibar jiki. 
A bayanin masana ba wani motsa jiki da zai sa irin wannan ba tare da duk jiki ya mori alfanun ba. Misali, motsa jiki na lilon kwance na daga kafafu ko kai wanda wasu suke ganin yana rage tumbi, ba tumbin kawai yake ragewa ba, yakan kara karfin damtsen cinyoyi da na gadon baya.
Ba kuma dole sai jiki ya ji zafi ba ne akan ce an motsa shi, da farko-farko masu motsa jiki sosai za su iya jin dan ciwon cinyoyi ko agara ko damtsen hannu, amma bayan ’yan kwanaki idan wurin ya sabe bai kamata a sake jin wani ciwo ba. Jin gajiya bayan motsa jiki ba matsala ba ce, tunda hakan ma ake so. 
Amma duk wani sabon ciwo mai radadi da hana sakat da aka ji kamar a cinyoyi ko a kirji, a bar motsa jiki a huta, idan bai tafi ba a je a ga likita.

Muhimmiyar Shawara Ga Baba Buhari Domin Ceto Kasarmu Nijeriya

Muhimmiyar Shawara Ga Baba Buhari Domin Ceto Kasarmu Nijeriya.
*Ya Kamata Canji Ya Soma Daga Majalisa
* Sanata na karbar Naira Miliyan 36,000,000 kowane wata*. 

Idan aka raba gida biyu yana karbar Naira Miliyan 18,000,000, ragowar *Naira Miliyan 18,000,000 za a iya amfani da su wajen daukar ‘yan Nijeriya 200 aiki kowa ya rika daukar albashin Naira Dubu 90,000 kowane wata.* 

Idan aka yi mutum 200 sau adadin Sanatocin mu 109 hakan na nufin za a dauki ‘yan Nijeriya *dubu 21800 aiki *. 

A takaice ‘yan Nijeriya 200 za su iya rayuwa a wadace da rabin albashin Sanata na kowane wata. 

*Dan Majalisar Wakilai na karbar albashin Naira Miliyan 25,000,000 kowane wata.*

Idan aka raba albashin gida biyu ya zama Naira Miliyan 12.5million a wata. Ragowar *Naira Miliyan 12.5 za ta isa a dauki ‘yan Nijeriya 135 aiki su rika daukar albashin Naira dubu 92,500 a wata*. 

‘Yan Nijeriya 135 sau adadin yawan ‘yan Majalisar Wakilai 360, hakan na nufin za a dauki ‘yan Nijeriya *dubu 48600 aiki*. 

‘Yan Nijeriya 135 za su rasu a wadace da rabin albashin dan Majalisar Wakilai.

 *Don haka Baba Buhari gwamnatin ka za ta iya daukar ‘yan Nijeriya dubu 70,400 aiki da za a rika ba su albashin Naira dubu 90,000 wasu kuma Naira dubu 92,500. Kuma cikin ruwan sanyi ta hanyar RABA ALBASHIN Sanatoci da ‘yan Majalisar Wakilai!!*

Ka gwada yin wannan lissafin ya mai girma Shugaban Kasa….

Yanzu aikin kowane dan Nijeriya ne ya yada wannan sako domin Sanatoci da ‘yan Majalisar Wakilai su san a dalilin albashin da suke dauka mutane nawa ne ba su da aiki a Nijeriya..

Ya kamata SAUYI ya fara daga MAJALISA!

ALLAH YA TAIMAKI NIJERIYA

Daga shafin Sarauniya

Fuel Subsidy Removal and the Tough Economic Situation in the Country

It’s been a couple of days now and the rate at which Nigerians are talking on social networks about fuel subsidy removal and the current difficult economic situation in the country is still on the rise. With respect to that, I found this write-up interesting and worthy of reading by Dr Ibrahim Idris of the faculty of science, Bayero University, Kano and the Nigerian blogger Dr Aliyu U. Tilde. 

I still believe and trust that PMB is a leading figure among the present defenders of the common man. He is however, up against a powerful cabals, mafias, world economic gladiators and all sort of bigots. Coupled with fervent prayers, we should give him some helping hands to at least lead us out of the doldrums. PMB may not be our last bastion of hope, sincerity and integrity but he is a force to reckon with any day as per the aforementioned are concerned.

– Ibrahim Idris

It is unfortunate that attempts are made to silence the voice of reason by the President’s supporters. The good thing is that strike or no strike, we will collectively pay for the price, supporters and opponents of the fuel price hike alike. In acca za ta sha rana, matankadin mazai sha.

IMF, World Bank and the West generally will never be on our side. They depend on our resources to survive. Our economic relationship with the West has been in inverse form for the past 400 years. There is nothing to convince me that it has suddenly changed, no matter how many times Cameron receives Buhari.

The Naira will soon be devalued, as hinted by Sahara Reporters, to N280 per dollar and VAT increased from 5% to 15%, in a country where nothing works and corruption in public service is the norm. IMF has demanded it as a condition to giving its $3 billion loan. That is the same N280 figure that was used to arrive at N145/liter of petrol as contained in Osinbajo’s defence of the subsidy removal debate.

Hard working citizens will be robbed of their earnings and officials will continue with their usual theft and opulence. Our good Buhari cannot stop them. He must have realized that now. If he could, he would not have gone to the IMF. Past governors alone can yield more than he needs. But they are working free. The trial of Saraki alone is taking ages and tells a lot about the weaknesses of our judicial system. That is the system we have in place today. It supports corruption and the President can do little about it, no matter the rhetoric. The Senate will not change the rules to the detriment of most of its members.

More tax and inflation inducing measures like devaluation and hike in fuel price without any subsidy even in agriculture in a corrupt country like Nigeria can only result in one thing: more poverty, more poverty and more poverty, beyond the present 70%. The present minimum wage of $90 per month will in the end be reduced to the value of $45 or less. But surely, there will be a lot of money raked from common citizens to finance the lavish lifestyle of the political class – from the President down to the councillor. As for the common man who is not enjoying even the minimum wage and not even a bag of fertilizer for his farm, his life will be continue to be unbearable. 

Poverty in turn cancels other things – education is one of them – and breeds other ills – like crime and the insurgency that we are just coming out of. And write it: This will not be the last hike in fuel price. The Naira will continue to fall and the need for an upward review of fuel price will soon and always be there, ad infinitum. It has happened many times in the past 42 years. The old gramophone plate of benefiting masses will be played again.

So in the end, one wonders who actually benefits from these measures. We are just banking on promises and promises – that the President will deliver. With the corrupt officials and politicians, one must learn not to squander his hopes.

Meanwhile, take your bearings from the mood of the marketers, whose two renown members, the Minister and his godfather, TYD, directs policy matters on petroleum. The marketers are happy like never before. But I f you see hyaenas rejoicing, be rest assured that the sheep is in trouble.

That is the British model of subjugation. It works by corruption and defending it through corrupt officials and institutions. The crude French does it directly from day one through the terms on which they gave independence to their colonies. All the national earnings of our Francophone brothers – except Guinea Conakry – are in the central bank in France and they cannot spend a penny or enter into any contract with any other nation without its approval. It prints and determines their currency. It approves their budget, every year.

The issue here is not Buhari the person at all. It is the same old West versus us. I have never been comfortable with his romance with these suckers. Neither am I comfortable with their praises of him. In ka ga kura na yabon dan maraki, cinye shi za ta yi.

May God have mercy on the darling of my heart, the Buhari of 1984-85. He is gone. He was full of energy and stood against them. He refused to devalue the Naira and was ingenious enough to get round the problem. The West and its stooges brought him down as they brought down Murtala when they could not bend him. I thought that Buhari was still around. Now I understand that he is no more. They kept his body but replaced his spirit with another one.

When they realized that they cannot prevent the trust that the common man has for the new Buhari, they courted him again and again. They have now come forward to use his position to achieve what they could not even achieve during Abacha, Obasanjo, Umaru and Jonathan.

May God forgive the present Buhari that has found himself amidst APC wolves and the corrupt governors that are eager to get the money to squander, seeing that present oil proceeds cannot satiate their greed. He does not have the free hand of the military leader of his old self. These wolves, as reported, surrounded him and pressed him into conceding to increase in fuel price, devaluation of the Naira and other measures stifling to the life of the common man. He ran and ran against such a day, but he could not run forever. No excuses now, though. As President, he knows, he must shoulder the responsibility. May God forgive him.

May the souls of past defenders of the common man like Dr. Yusuf Bala Usman, Malam Aminu Kano and General Murtala Muhammed continue to live in peace. The common man will continue to suffer in your absence. Crass capitalism, IMF and the World Bank are having a field day in your beloved country. We miss you today.

Dr. Aliyu U. Tilde

Between Sanusi Lamido Sanusi and Goodluck Jonathan

Hello folks! I found this article amusing. It keeps one going on and on and on until the end of the corruption-concerned situation. Enjoy reading it now, feel bad later…

If Jonathan is not arrested, President Buhari’s fight against corruption is just window dressing! please read:
Sanusi, as central bank governor, had written to former president Goodluck Jonathan in 2013 to raise the alarm over billions of dollars from oil sale not remitted to the federation account.
Sanusi was later suspended as CBN governor but he became emir of Kano while he was in court seeking that his suspension be declared illegal.
The emir of Kano revealed that Jonathan did nothing until former President Olusegun Obasanjo wrote his own letter.
Amaechi on Wednesday night confirmed to TheCable that he was the one that leaked the letter “because the corruption was simply too much”.
JONATHAN SAID I LEAVE OR HE LEAVES
Narrating the $20 billion saga to Forbes Africa, Sanusi said that in 2012 and 2013, government revenue collapsed by $10 billion, without a collapse in oil prices or production capacity, adding that the CBN found a $49 billion revenue gap.
Shocked at the revelation, Sanusi said he wrote Jonathan, saying: “If this continues, we are going to have a big problem if the price of oil came down. We can’t protect interest rates, we can’t protect exchange rates, we can’t protect reserves.
“We may have to tighten money to prevent inflation, there will be unemployment, government will suffer – all of the things we are seeing today.
“In the middle of all these, the president called me and said I should see him at 3pm. I turned up at 3pm and the entire place had been swept. There was no one apart from security services. I got to his office, it was just me and him. It was as if everybody had been asked to go.
“And so he says to me, he’s calling me because he is surprised that letter I wrote to him got to Obasanjo, I said I’m surprised too.
“He said he’s convinced that the letter went from the central bank to Obasanjo, and I had 24 hours to find who leaked the letter or sack somebody; the director who prepared the letter or my secretary and if I did not sack them, that was proof that I leaked the letter and therefore, I should resign.
“I said to him that I’m surprised that I’m being asked to resign for raising an alarm over missing funds and the minister in charge of the portfolio is not being asked to resign.
“From then I knew I had signed my equivalent for death warrant. But I said I was not resigning. He got very angry and said whether you like it or not, you’re going to leave that office, I cannot continue to work with you, either you or I will leave government.”
JONATHAN IS NOT A LEADER THAT CAN KILL
“I was amused that leaking the letter is far more crime than leaking money. I went straight to the office of the principal secretary to the president, and I met him with a gentleman from Kano, who was foreign minister Ambassador Aminu Ali.
“I said to them, gentlemen, I’m coming to you because I just had a meeting with the president, and there were no witnesses, and the president had threatened me.
“I repeated what happened and told them I am going to tell people close to me, if anything happens to me, it is the president.
“I don’t think I was really in fear of my life. Even if you don’t like someone – Jonathan was not the kind of person that would have someone killed. He wasn’t that kind of leader.”
BEN BRUCE TOLD ME THEY’D JAIL ME
“I remember Ben Murray Bruce, who is now a senator, coming to me to say that he had it on good authority that if I went to the senate with my documents, I would be removed, investigated and imprisoned.
“Then I said, why would I be imprisoned, and he said, you know, you’ve worked in government. I have worked in government, if people really want to find something on you, in the central bank, five years, they would come and look, they would find something.
“I was like they would find it if I have done it. I mean they can plant something, but if haven’t done it, maybe somebody under me had done something that I wasn’t aware of.
“But in all my years at the central bank, to the best of my knowledge, I had done nothing that should put me in prison. However, I said to him, tell the president, from me, that if the punishment for going to the senate is prison, he doesn’t need to go through all of that, just ask him to tell me what prison he wants me to go to and for how many years, I’d drive myself there.”
OBASANJO’S LETTER PUSHED JONATHAN TO ACTION
Sanusi said nothing was done until Obasanjo wrote his famous open letter to Jonathan. In that letter, he now referred to a letter from the central bank governor.
“This was in August 2013, the president received the letter and did nothing. A few weeks after that, the finance minister called to say, governor, can we do some reconciliation on oil revenue numbers? I said minister, I report to the president.
“I have written to the president, if the president wants me to sit with you and do reconciliation, the president will tell me.
“After Obasanjo’s letter, all hell now broke loose. The letter was then leaked to online media, and it became public. That was when the president got angry and we then had to sit and do reconciliation.
NOBODY TOUCHES DIEZANI AND SURVIVES
“I knew that taking on NNPC was taking on the most powerful minister in Jonathan’s government, and nobody who had touched Diezani had survived. It was not a question of what would happen, I just didn’t care at that time. I did not want to go down in history as having seen this and kept quiet.
“After the first round of reconciliation, there was $29 billion that was explained. And how was that explained? Crude that was shipped by NNPC did not entirely belong to NNPC.”
He said some oil companies paid taxes and royalties in oil, and the NNPC sold this oil on behalf of FIRS, meaning FIRS got the money and not necessarily the federal government.
“No reasonable explanation for $20 billion, $6 billion was with NPDC that had not gotten to the federation account till date.”

In Ba Tsaida Doka, Ba Canji (1)

In Ba Tsaida Doka, Ba Canji (1)
Na Dr. Aliyu U. Tilde
Tafiya ta fara kankama, mun fara shiga jarrabawa a canjin da akasarin masu zaɓe suka buƙata a 2015 yayin da suka zaɓi jami’iyya mai ci yanzu, watau APC, a matakai dabam dabam, amma musamman na Shugaban Ƙasa inda suka zaɓi Muhammadu Buhari, Yayana. Mu kam dama mun yi shekara 16 ke nan muna rubuce-rubuce kan jama’a su tashi a kawo canji. Alhamdulillahi, abin da ya rage yanzu shi ne canjin ya tabbata.
Amma tun kafin a je ko’ina, sai ga wasu abubuwa suna faruwa. Misali, shekaranjiya jaridar Daily Trust ta buga labarin yanda majalisa suke watanda da kuɗin jama’a, inda suka sayi jip-jip guda 108 a farashin kasha-mu-raba. Ga su kuma suna ƙoƙarin canza doka don su yi wa shari’ar da ake wa shugabansu Bukola Saraki ƙafar angulu. Ga joji-joji da lauyoyi sun daina cin hanci. Ga ƴan kasuwa na fetur da uwa-uba ma’aikata suna cin karensu ba babbaka wajen gasa mana aya a hannu. Ga jami’an tsaro na ci gaba da karɓar cin hanci a hanyoyi da ofisoshi da bai wa masu laifi haɗin kai. A ƙarshe, muma talakawa masu ƙin doka a cikinmu sun saki jiki kowa na abin da yake so. Kai ka ce ba Buhari ba ne a kan mulki.
A dandalolin sada zumunta, sau da yawa hayaniya takan kaure tsakanin mutane kan yadda gyaran ya kamata a yi shi, da kuma ko yakamata a ɗorawa Buhari laifi na rashin nuna isasshen tsananin da ya kamata don hana miyagu cigaba da tabka ta’asa.
Wasu suna ganin sai mu ƴan Nijeriya mun gyara kanmu ne kasar za ta gyaru. Wasu na ganin cewa yakamata Shugaba ya jagoranci gyara ta hanyar inganta hukumomin tsaro da tilasta wa jami’ansu wanzan da doka.
Hujjar kashin farko ita ce Yaya Buhari ba zai kasance a ko’ina ba. In mun azuma muka ce za mu tsai da munanan ayyukanmu, to canji zai samu cikin ruwan sauki. In ba haka ba, komi ya yi a cikin ofis dinsa, a can sama, Yaya Buhari ba zai iya canza na kasa ba. In canjin nan bai yiwu ba, masu wannan ra’ayin suna ganin laifin mu talakawa ne don ba mu tashi tsaye ba.
Misalin wannan ra’ayin shi ne na karanta ɗazu lokacin da wani makaranci ya yi ta’aliƙi a shafin Facebook na Dr. Sheriff Almuhajir, bayan Doktan ya liƙa wani bidiyo na wata a-kori-kura da take shirin pakawa don a zuba mata fetur a cikin wasu maka-makan duron a gidan man NNPC (Megastation) na Damaturu. Ga abinda makarancin ya ce don waƙa a bakin mai ita ta fi daɗi: 
“Yanzu jama’a idan za muyi ma kanmu adalci ina laifin Buhari anan? Wannan duk irin abunda ke faruwa ne a kowanne gidan mai fadin kasar nan… Imagine, ga yan sanda, civil defense and other security agencies, station manager and pump attendants, ga jamaar gari kuma haka yana faruwa. Walahi muke azabtar da kanmu. Muke jawo ma kanmu masifa muna yima shuwagabanni sharri domin son rai… Yanxu don Allah a haka zamu gyara kasar nan? Don Allah a haka zamu dunga zagin Buhari bacin muke haddasa ma kanmu fitina?
Bari mu yi nazari mai ɗan zurfi a kan wannan ra’ayin kafin mu je kan ra’ayi na biyu a kasha na biyu na wannan sharhin.
To idan ba inda talakawa aka jagorance su suka yi juyin juya hali ba – watau revolution – yana da wuya a ce a tarihi akwai yadda aka kawo canji a tsarin demokradiya mai tsarin doka ta hanyar bijirewar talakawa. Ko an samu wani canji, na ɗan lokaci kaɗan ne kawai. Daga nan azzalumai za su dawo da cin karensu ba babbaka. To, in ma talakawan sun cije a wani garin, a wani ba za su cije ba, kuma tsara su yadda za su cije din su yaƙi zalunci a ƙasa baki ɗaya ba ƙaramin aiki ba ne. Haka kuma, in sun cije a kan cuwa-cuwar man fetur, ya za su yi da sauran fannonin rayuwa?
Iya sanina, ɗan adam yana iya tsaida shawara a ƙashin kansa ya daina laifi. Hakan yakan faru da mutane ƙalilan waɗanda Allah ya nufa da shiriya ko kuma ɗan Adam ɗin wayewarsa ta kai ya ma kansa karatun ta-natsu, amma ba zukatan mutane su gamu a lokaci guda su yarda cewa za su gyaru ba. In ba doka aka tsaida ba, ko aka kawar da dalilin da ya jawo aikata laifin – kamar a wadatar da mai a ko’ina – to fa akwai ƴan Adam da yawa a ƙasashe dabam dabam da za su gwada yin laifi ta yadda za su biya wa kansu buƙata, Allah bashin sauran mutane su ci gaba da wahala. In doka bata tsaida su ba, to fa za su zarce, su dauwama akan laifi har wasu su kwaikwayesu.
Dalilin wannan shi ne tabi’ar ɗan adam da Allah ya hallice shi da ita, kamar yadda ya faɗa a Alqur’aninsa maigirma, cewa ɗan adam na son aikata ɓarna (Al-Kiyamah), mai matukar son dukiya ne (Al-‘Adiyaat), mai handama ne (Al-Isra ) da sauran ayoyi. Inda duk abu ya zame halitta, to fa kau da shi a taron mutane sai an shirya.
Wannan shiri shi ne tsara doka da wanzar da ita. Ai ka ga da tsarin dokokin addini aka tarbiyattar da mutanen jahiliyya har suka zame mutanen kirki, suka gina al’umma mafificiya mai dokoki da tsare-tsaren tafiyar da lamurran ɗan Adam. Haka kuma da daular musulunci ta bunƙasa ta kai ga Sham da Farisa, sai suka ci gaba da aiwatar da tsare-tsaren aikin hukuma da abinda suka iske ana yi a waɗannan kasashen. Shugabannin ba su bar mutane da imaninsu ba kawai. A’a. Sun ɗora su ne bisa doka har kowa ya saba. Mai laifi a hukunta shi, mai biyayya a sama masa sarari. Ko Zul-Ƙarnaini ma haka ya yi (Al-Kahf ).
A yau, akasarin mutane suna son doka suna bin ta albarkacin addini da wayewar ɗan adam, ko tsoron horo ko tsammanin samun amfani daga bin dokar. Amma a cikin kashi ɗari, dole sai ka samu kashi biyar ko ƙasa da haka na waɗanda suke son aikata laifi, su take doka don su biya bukatarsu in sun samu dama. Da farko za a yi doka, a sanar da ita kuma mutane da yawa za su bi ta. Amma don an san akwai waɗancan tsirarun da za su karya doka, sai aka dauki jami’an tabbatar da doka da zaman lafiya (law enforcement agents, jami’an tsaro). Doka ta kowa da kowa ne, amma jami’an tsaro na masu karya doka ne. In ba ka yi laifi ba, ba ruwanka da dansanda. Don haka bahaushe ya ce, kowa ya kwana lafiya shi ya ga dama.

 

Don haka zan rufe wannan kasha na farko da cewa a kafaffiyar ƙasa, wayayyiya, mai bin tsarin demokraɗiya da sanin haƙƙin ɗan adam, yana da wuya dukkan mutane su taru a kan bin doka bisa rajin kansu. A kullum masu laifi na nan wanda basu da yawa in ana aiwatar da doka, amma suna da yawa in jam’i’an tsaro ba sa aikinsu.
Daga wannan fuskar, sai muce ba a ɗorawa mutanen Yobe zuwa su hana saida wa ƴan bumburutu mai a gidan mai ba don yin haka yana da kamar wuya kuma zai iya haddasa fitina fiye da ta rashin man. Jam’i’an tsaro ne ya kamata a matsawa su aiwatar da aikinsu wanda ake biyansu albashi a kai kuma wanɗanda suka rantse za su yi. In suma sun ƙi yin haka, to kallo dole ya koma sama, kamar yadda za mu gani a kashi na biyu na wannan maƙalar.
Sai mun sadu anjima. Bari mu yi azahar.
18 April 2016

Ciwon Daji (Cancer) Sai Addu’a

My sister, Hussna is being ravaged by breast cancer. She’s one of the strongest girls I know. She’s battling it out like the quintessential Amazon that she is. May Allah heal her. May Allah ease her pains, amin. 
So I saw this on the wall of my brother Eric Henderson and I thought it very apt. You too can share for the sake of all those battling with cancer. May Allah ease their pain. 
“I know what cancer and treatment can do to a body and mind as I’ve watched the transformation. I sometimes wonder if the treatment is worth it in the long haul. With a heavy heart today especially. Nothing is more painful than watching someone at the end of their life because of cancer. Trying to look good, but after chemo and radiation … you know the person is physically changed and they’re in shock. I know many of you do not give a hoot about this message because, of course, the cancer has not touched you. You do not know what it’s like to have fought the fight or had a loved one who leads a battle against cancer. For all the men and women I know, I ask you a small favour and only some of you will do it. If you know someone who has led a battle against cancer, still struggling or who passed, please add this to your status for one hour as a mark of support, respect and remembrance. Copy and paste to support those affected by cancer. From your phone or tablet, hold your finger on the message to copy and paste on your page !!”

FITATTUN TAURARUN KANNYWOOD 10 A TWITTER DA INSTAGRAM 2015

A ƙarshen shekarar 2014, mun yi ƙoƙari sosai wajen zaƙulo fitattun jaruman masana’antar finafinan Hausa wato Kannywood. A wannan shekarar ma dai ba mu gaza ba domin mun tsaya mun yi kyakkyawan bincike wajen gano muku fitattun taurarun a kafafen sada zumunci na Twitter da Instagram.A shekarar 2015 ma dai abubuwa da dama sun faru a kafafen sada zumuncin na Intanet kama daga tashe-tashen hankali da ƙungiyar boko haram ke kawowa, zaɓen shugaban ƙasa da aka yi da samun nasara da Shugaba Muhammadu Buhari ya yi har i zuwa ɓangaren nishaɗi da ɗeɓe kewa musamman ma a masana’antar Kannywood ɗin inda kamar kullum manya-manyan jarumai kamar su Ali Nuhu, Hadiza Gabon, Adam A Zango, Nafisa Abdullahi da sauran su suka taka rawar gani.

Ga yadda lissafin ya canza a masana’antar ta Kannywood musamman ma duniyar Instagram.

A Twitter 

10. Yakubu Mohammed

Yakubu Mohammed shi ya zo na 10 a wannan shekarar in da ya ke da mabiya kimanin 19.1k. A shekarar 2015 dai shi ne ya zo na 9 amma duk da ya samu ƙarin mabiya 10k bai kai ga tsayawa a na taran ba ko kuma ƙasa da haka. 

Yakubu Mohammed

 

9. Bello Muhammad Bello

General BMB ya zo na 9 a wannan shekarar inda ya ke da mabiya 22k. Ya motsa dan a shekarar 2014 shi ne na 10 a inda ya ke da mabiya 9.8k. Hakan ya nuna ya samu ƙarin mabiya 12.2k a cikin shekara ɗaya. 

General BMB da sabon irin wankan da ya shigo da shi

 

8. Fati Washa 

A wannan shekarar ma dai Fati Washa ta riƙe kambun ta na 8 a jerin taurarun da suka fi kowa yawan mabiya a Twitter in da ta ke da mabiya 25.2k. Fati ta samu ƙarin masoya har 13.4k a cikin shekara 1.

7. Mal. Aminu Saira
Mal. Aminu Saira ya na ƙoƙari sosai a ko ina. Duk da wannan shekarar ya sakko daga na 6 ya koma na 7 a inda ya ke da mabiya 28.1k. Babban Darakta dai ya samu ƙarin mabiya 10.8k a wannan shekarar.

Babban Darektan Kannywood kenan

 
6. Sani Musa Danja

Sani Danja ma dai ya sakko daga na 4 a shekarar 2014 zuwa na 6 a wannan shekarar duk da cewar ya samu ƙarin mabiya 9.6k. Danja ya na da mabiya 32.4k a Twitter.  

Wannan shekarar an dama da shi a Nollywood sosai

5. Hadiza Aliyu Gabon

Hadiza Gabon ta yi tashin gwauron zabo in da daga na 7 a shekarar 2014 zuwa na 5 a wannan shekarar da mabiya 33.3k. Gabon dai ta samu ƙarin mabiya har 17k a wannan shekarar. Gaskiya tauraruwar ta na haskawa a ko ina ba ma sai Intanet ba.

4. Nafisat Abdullah

Nafisa dai wannan karon ta yi ƙasa a Twitter in da ta zo na 4 da mabiya 37k ba kamar waccen shekarar ba da ta zo na 3. Ƴar gayun Kannywood dai ta samu ƙarin mabiya har 14k a shekarar 2015.

3. Rahama Sadau

Itama Rahama Sadau ta yi tashin gwauron zabo in da daga na 5 a waccen shekarar ta 2014 zuwa ta 3 a wannan shekarar ta 2015. Rahama ta samu ƙarin mabiya har 21.9k.

2. Maryam Booth

Maryam Booth tananan a matsayin ta na 2 a jerin taurarun da suka fi yawan mabiya a Twitter. Booth dai ta samu ƙarin mabiya har 13.7k. 

1. Ali Nuhu

Ali Nuhu ma dai wannan shekarar shi ya fi kowa yawan mabiya a Twitter Kannywood in da ya ke da mabiya 83k. Sarki Ali ya samu ƙarin mabiya 24.5k. Wannan ya nuna shi ya fi kowa samun mabiya a shekarar 2015 kuma shi ne jarumi na farko a Kannywood da aka fara tantancewa a Twitter.
A Instagram 

10. Saddiq Sani Saddiq

Wannan karon ma SSS ya na nan a na goman shi in da ya ke da mabiya 55.3k. SSS ya samu ƙarin mabiya 48.8k a shekarar 2015.  

SSS a Jos kwanannan

 

9. Aisha Tsamiya

Aisha Tsamiya ta sakko daga na 8 zuwa na 9 a wannan shekarar inda take da mabiya 57.8k. Aisha ta samu ƙarin mabiya har 50.1k a shekarar 2015.  

Aisha Tsamiya

  
8. Halima Atete

Atete ta samu damar haurowa jerin taurarun da suka fi kowa yawan mabiya a masana’antar Kannywood a duniyar Instagram inda ta ke da mabiya har 68.9k kuma ta bama Aisha Tsamiya ratar 11.2k! Atete ta riƙe wuta tana bin ƴan-uwanta bomfa-to-bomfa gaskiya.  

Halima Atete

 7. Adam A Zango

Adam Zango ya sakko daga matsayinsa na 6 zuwa na 7 a wannan shekarar inda yake da mabiya 79.9k. Prince Zango ya samu ƙarin mabiya 70.4k a cikin shekara ɗaya.  

Adam A Zango

 
6. Fati Washa

Fati Washa tana ɗaya daga cikin fitattun taurarun Kannywood 10 a Twitter da Instagram. Washa ta nada mabiya 91.1k kuma ta samu ƙarin mabiya 83.1k. Washeshiyar Yarinya (*dariya)  

Fati Washa

 
5. Nafisa Abdullahi

Nafisa Abdullahi tananan a na 5 ɗinta kamar shekarar data gabata inda take da mabiya 96.6k. Ta samu ƙarin mabiya 86.6k a cikin shekara 1.  

Ƴar gayun Kannywood!

 
4. Maryam Booth

Maryam Booth ta sakko sosai daga Sarauniyar Instagram wato na ɗaya a 2014 zuwa na huɗu a wannan shekarar inda take da mabiya 111k. Maryam Booth ta samu ƙarin mabiya 84.9k.  

Maryam Booth

 
3. Ali Nuhu

Ali Nuhu yana nan a na ukun shi ma a wannan shekarar inda yake da mabiya 116k. Ya sami ƙarin mabiya 94.6k. Ba mu yi bincike ba a Facebook amma dai yanzu haka Ali Nuhu ya na da mutanen da ke bibbiye da al-amuran shi a Facebook din kusan 705.45k wanda hakan ke nuna cewa ya samu ƙarin masoya 341k a wannan shekarar. Harshashe ya nuna a shekarar 2016 Ali Nuhu zai samu masoya miliyan ɗaya.  

Sarki shi ne Kannywood!!!

 
2. Rahama Sadau

Rahama Sadau ta ƙara tashin gwauron zabo a Instagram ma inda ta zo na 2 daga na 4 a waccen shekarar inda yanzu haka take da mabiya 130k. Rahama ta samu ƙarin mabiya 110.4k a wannan shekarar!  

Rahma Sadau ranar birthday ɗinta

 
1. Hadiza Aliyu Gabon

Hadiza Gabon ita ce Sarauniyar Instagram ɗin Kannywood a wannan shekarar inda take da mabiya 134k. Gabon dai ta samu ƙarin mabiya har 111.9 wanda hakan ya nuna tafi kowa samun mabiya a wannan shekarar.  

Tauraruwar Gabon na haskawa sosai

 Mun gode ƙwarai da gaske. Ku bi shafin mu na Twitter, InstagramFacebook da kuma Tumblr 

#RanarHausa ta Samu Karɓuwa 

Daga Suleiman Garba Sule (Emlanis)

Ranar Hausa, 26 ga watan Agusta, rana ce ta musamman da aka ware dan ɗaukakin ilahirin Hausawan dake kafafen sada zumunta na yanar gizo musamman Twitter, su nuna ma duniya daraja, ƙarfi da ƙimar yaren su ta hanyar turo da duk tweet ɗinsu tare da tambarin abin batu na #RanarHausa.

An samu nasara sosai domin ko Hausawa da dama sun nuna kishi da alfahari da yaren nasu ta inda suka (suke a halin yanzu haka) tattauna muhimman abubuwa da dama kama daga karin magana, marubuta da littattafan Hausa, mawaƙa da masu wasan kwaikwayo na da da na yanzu, masarautun Hausa, al-adu da dai sauransu. A taƙaice dai #RanarHausa ya shiga jerin manya-manyan abubuwan da aka fi tattaunawa a Najeria wanda shi ne babban burin mu dan ta haka ne abin zai bazu ta ko ina.


  
  
  
  
  
  
  
  
  
  

Waƴanda suka fara ƙirƙiro da Ranar Hausa sune @Bahaushee , @dawisu, @Mutan_arewa, @HausaTrends, @HausaPictures, @Hausa24com da dai sauransu ƴan ƙungiyar Arewa Bloggers Forum.


Manya-manyan ƴan jaridu da masu faɗa aji kamar su Aminu Gamawa, Mansur Liman, Omojuwa, Bashir Ahmad, Aliyu Tanko, BBCHausa da dai sauran su, sun tofa albarkacin bakin su a wannan biki mai ɗinbin tarihi da aka fara yau.

Kubi shafukan mu na Twitter @HausaTrends, @HausaPictures, @HausaLovebirds, @HausaFacts_, da @ZaurenLabarai. Zakuma ku iya bin mu a Instagram, Facebook da kuma Tumblr. Mun gode 

Wasu Hadaddun Hotunan Zahra Buhari

20150116-220210.jpg
Ainihin hoton da ya jayo hankalin matasan Najeriya akan Zahra Buhari, yar gidan General Muhammadu Buhari. Da kuma wannan

20150116-220844.jpg
Da wannan…

20150116-220944.jpg
Ita dai Zahra takai kimanin tsawon kwana uku kenan sunan ta ya na jerin Trending Topics a Najeriya ba dan komai ba sai saboda wa yan nan hotunan nata da kuma wata kila wannan…

20150116-221511.jpg
Da wannan wanda ta ke tare da kyakkyawar mahaifiyar ta…

20150116-221708.jpg

Sai dai akwai wasu wa yanda ba su zagaya duniya sosai ba. Wa yan nan kuwa su ne…

20150116-222013.jpg

20150116-222036.jpg

20150116-222059.jpg

20150116-222132.jpg

20150116-222154.jpg

20150116-222218.jpg
Babban abinda ya bawa matasan Najeriya kudu da arewa sha’awa shi ne Zahra Buhari ta samu daukaka nan da nan ta hanyar yaduwar da hotunan ta suka yi ba tare da ta nuna tsiraicin ta ba hatta gashin ta. To da ya kuke tunani? Ai dole a samu yayan General Muhammadu Buhari da tarbiya duk da dai ita rayuwa haka take duk tarbiyar da ka ba dan ka wani zai iya tanbarewa, amma zai wuya ga yayan GMB.

Previous Older Entries